Gwamnatin jihar Kano ta sanar da ranakun komawa makaranta

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana ranar Lahadi 6 ga Afrilu, 2025 a matsayin ranar komawa makaranta ga ɗaliban makarantun kwana na gwamnati da masu zaman kansu, a matakin firamare da sakandare, domin cigaba da zangon karatu na uku na shekarar 2024/2025.

Yayin da ɗalibai a makarantun jeka Ka dawo a faɗin jihar za su koma makaranta a ranar Litinin 7 ga Afrilu, 2025.

Dambarwar Rivers: AIG Gumel ya gamu da fushin Sufeto Janar na yan sandan Nigeria

Wata sanarwa daga Daraktan Wayar da Kai na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru, ya bukaci iyaye da masu kula da ɗalibai da su lura da ranar komawar makaranta domin tabbatar da bin wannan umarni gaba ɗaya.

InShot 20250309 102403344
Talla

Sanarwar ta ambato Kwamishinan Ilimi, Dr. Ali Haruna Makoda, yana jaddada cewa za a ɗauki matakin ladabtarwa ga duk wani ɗalibi ko ɗaliba da ya ƙi bin wannan umarni.

Ya shawarci ɗalibai da su guji kawo haramtattun abubuwa irin su wuka, reza ko miyagun ƙwayoyi zuwa makaranta, tare da zama masu bin doka domin samun nasara a karatunsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...