Dambarwar Rivers: AIG Gumel ya gamu da fushin Sufeto Janar na yan sandan Nigeria

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Babban Sufeton ‘yan sandan Nigeria, Kayode Egbetokun, ya mayar da Mataimakinsa da ke kula da Yankin Zone 7 Abuja, Usaini Gumel, zuwa Sashen Hulɗa da Jama’a, Bincike da Tsare-tsare, bisa zargin cewa ya bayyana ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Rivers da kuma dakatar da Gwamna Sim Fubara a matsayin abin da ya saɓawa kundin tsarin mulki.

Rahotanni sun bayyana cewa Mista Gumel ya faɗi ra’ayinsa kan dokar ta-ɓaci ne a cikin ofishinsa yayin wata tattaunawa da wasu daga cikin abokan aikinsa, amma ɗaya daga cikinsu ya tona masa asiri ya kai rahoto ga babban Sufeto Janar.

InShot 20250309 102403344
Talla

AIG Gumel, wanda ya fara aiki a Zone 7 Abuja a ranar 19 ga watan Fabrairu, bai samu wata takardar tuhuma ko gayyata don kare kansa a hukumance ba kafin a tura shi zuwa sabon sashen.

Gwamnan Kano ya bayyana dalilin da yasa ya sake dawo da Sarkin Gaya

Yayin da Zone 7, wacce ke kula da Babban Birnin Tarayya da Jihar Neja, ke da matakin aiki mai muhimmanci da kuma ɗaukaka, ana kallon Sashen Hulɗa da Jama’a, Bincike da Tsare-tsare a matsayin wuri na ladabtarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...