Dambarwar Rivers: AIG Gumel ya gamu da fushin Sufeto Janar na yan sandan Nigeria

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Babban Sufeton ‘yan sandan Nigeria, Kayode Egbetokun, ya mayar da Mataimakinsa da ke kula da Yankin Zone 7 Abuja, Usaini Gumel, zuwa Sashen Hulɗa da Jama’a, Bincike da Tsare-tsare, bisa zargin cewa ya bayyana ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Rivers da kuma dakatar da Gwamna Sim Fubara a matsayin abin da ya saɓawa kundin tsarin mulki.

Rahotanni sun bayyana cewa Mista Gumel ya faɗi ra’ayinsa kan dokar ta-ɓaci ne a cikin ofishinsa yayin wata tattaunawa da wasu daga cikin abokan aikinsa, amma ɗaya daga cikinsu ya tona masa asiri ya kai rahoto ga babban Sufeto Janar.

InShot 20250309 102403344
Talla

AIG Gumel, wanda ya fara aiki a Zone 7 Abuja a ranar 19 ga watan Fabrairu, bai samu wata takardar tuhuma ko gayyata don kare kansa a hukumance ba kafin a tura shi zuwa sabon sashen.

Gwamnan Kano ya bayyana dalilin da yasa ya sake dawo da Sarkin Gaya

Yayin da Zone 7, wacce ke kula da Babban Birnin Tarayya da Jihar Neja, ke da matakin aiki mai muhimmanci da kuma ɗaukaka, ana kallon Sashen Hulɗa da Jama’a, Bincike da Tsare-tsare a matsayin wuri na ladabtarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...