Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Date:

Daga Sani Idris maiwaya

 

An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi ta jihar Kano da su fadada ayyukansu ta yadda za’a tallafawa al’umma wajen ba da Zakka yadda ya Kamata.

Mai Martaba Sarkin Kano na 16 Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu ne ya bayyana hakan yayin da ya karbi bakuncin ayarin shugabannin Hukumar Zakka da Hubusi ta jihar Kano a Fadar sa

Yana mai cewar bada Zakka na matsayin wata hanya ta sauke nauyi daga cikin rukunan Musulunci .

InShot 20250309 102403344
Talla

” Muna fatan za ku fadada aiyukan ta yadda mutane da yawa za su amfana da zakkar, dama manufar zakka ita ce kawarwa ko rage talauci a cikin al’umma”.

Sarki Sanusi II ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa don baiwa hukumar zakkar dukkanin wasu shawarwari da hadin kai da goyon baya don inganta aiyukansu.

A Jawabin Sa tun da Farko, Shugaban Hukumar zakka da hubusin Barista Habibu Dan Almajir ya ce sun kai ziyara fadar Sarkin ne don neman goyon bayan Masarautar Kano bisa irin ayyukan hukumar.

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

” Mun zo wannan fadar ne don neman shawarwari da goyon bayan mai martaba ta yadda za mu inganta aiyukan wannan hukumar.

Wakilinmu ya bamu labarin cewar Shugaban Hukumar Barista Habibu Dan Almajir ya Kuma yabawa Masarautar Kano bisa irin Tarbar da akayi Musu.

Shugaban hukumar zakka da hubsin Barr. Habib Dan Almajiri ya ziyarci Sarkin tare da Commissioner l Malan Nafi’u! Umar Harazumi Da Commissioner II Malan Ali Mustapha Kuraysh da Members tare Da Daraktocin hukumar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...

Yadda falakin Shinkafi ya sha ruwa da raba kayan sallah ga marayun da yake kula da su a Kano

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa     Falakin Shinkafi Amb Yunusa Yusuf Hamza,...