Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Date:

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin ƙasar na tsawon kwanaki huɗu.

Hukumar ta ce mutane za su ji sauyin al’amura a tsawon lokacin da za a kwashe ana tsala zafin ranar.

InShot 20250309 102403344
Talla

Jihohin da aka yi hasashen za su fuskanci ƙaruwar yanayi na zafin rana sun haɗa da Neja da Kwara da Oyo da Kogi da Nasarawa da kuma Benue.

Sauran sun haɗa da Enugu da da Anambra da Abia da Ebonyi da Cross River da birnin tarayya Abuja.

Yadda falakin Shinkafi ya sha ruwa da raba kayan sallah ga marayun da yake kula da su a Kano

Sai kuma Taraba da Adamawa da Plateau da Kaduna da Zamfara da kuma Sokoto.

Wata sanarwa da Nimet ta fitar ranar Litinin a Abuja, ta ce mutane su guji fita cikin tsananin zafi musamman daga karfe 12 na rana zuwa karfe 3.

Ta kuma shawarci al’umma da su riƙa shan isasshen ruwa a tsawon lokacin – su kuma yi amfani da fanka da na’urar sanyaya ɗaki da kuma zama a wurare masu inuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Yadda falakin Shinkafi ya sha ruwa da raba kayan sallah ga marayun da yake kula da su a Kano

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa     Falakin Shinkafi Amb Yunusa Yusuf Hamza,...