Dangote ne kadai zai iya karya farashin takin zamani kamar yadda ya yiwa man fetur a Nigeria – Falakin Shinkafi

Date:

 

 

Falakin Shinkafi Amb. Dr. Yunusa Yusuf Hamza ya yi kira ga shahararren dan kasuwa kuma attajirin Nahiyar Africa Alhaji Aiko Dangote da ya taimaka ya karya farashin takin zamani kamar yadda ya yiwa man fetur a Nigeria.

“Kamar yadda kowa ya sani dalilai uku ne su ka sanya aka sami hauhawar farashin takin zamani a Nigeria, na daya tsadar danyen mai a kasuwannin duniya, sai karewar darajar Naira akan Dala, da kuma kudin sufuru, kuma dukkan wadannan an sami sauki akansu don haka akwai bukatar takin shi ma ya sauka”.

InShot 20250115 195118875
Talla

Falakin Shinkafi ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da ya yi da jaridar Kadaura24.

Ya ce yadda farashin kayan abinchi ya karye a bana, akwai bukatar takin zamani shi ma ya yi sauki don manoma su sami damar yin noma a dumina mai zuwa.

An sake samu tsaiko a shari’ar neman a hana kananan hukumomin Kano kudadensu

“Mun ji manoma suna ta kukawa da karyewar farashin kayan abinchi, kuma suna kuka cewa taki har yanzu bai sauka ba, wanda suka ce hakan babbar barazana ce a gare su”. Inji Falaki

Amb. Yunusa Yusuf Hamza ya ce tabbas idan Alhaji Aliko Dangote ya taimaka aka sami saukin farashin takin zamani, to akwai yiwuwar farashin kayan abinchi su cigaba da sauka, wanda kuma hakan zai taimakawa talakawa sosai.20250228 181700

Ya ce kowa ya ga irin rawar da Dangote ya taka wajen rage farashin man fetur a Nigeria, kuma muddin ya taimaka haka za a sami sauki a bangaren takin zamani a kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

2027: Atiku Abubakar ya bayyana matsayarsa game da kasancewarsa a PDP

  Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin...

Cikakken Bayani Kan Yan Bindigar da Yansanda Su Ka Kama a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar yansanda ta kasa reshen jihar...

Gidauniyar Sheikh Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa magidanta 600 kayan abinchi a Kano

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Gidauniyar Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa...

Gwamna Abba Gida-gida Ya Kaddamar Da Gyaran Hanyoyi 17 A Babban Birnin Kano

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da...