Allah ya yiwa Sarkin Tsaftar Kano Rasuwa a Kasar Saudia

Date:

Daga Ibrahim Sani Mai Nasara
An sanar da rasuwar Sarkin Tsaftar Kano Alhaji Jafar Ahmed Gwarzo a yau Laraba.
 Alhaji Jafar ya rasu ne a yau bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya a kasar Saudiyya.
 Kafin rasuwarsa, Sarkin ya kasance babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje kan rigakafin cutar shan inna.
 Da yake tabbatar da rasuwar sa ga manema labarai, wani makusanci marigayin Alhaji Nasiru Sani Gwarzo ya ce, marigayi Jafar Gwarzo ya tafi kasar Saudiyya domin yin Umrah kwanakin baya.
 Marigayin ya rasu ya bar mata da ’ya’ya da dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...

An sake sauya lokacin jana’izzar Aminu Ɗantata – Gwamnatin Nigeria

Gwamnatin tarayyar Nigeria ta ce Hukumomi a Kasar Saudiyyar...

Fadan daba: ku fito ku Kare Kan ku da iyayenku – Gwamnatin Kano ga matasa

Ku tashi ku Kare kanku da iyayen Gwamnatin jihar kano...