Bayan Rahoton Kadaura24, Gwamnan Kano ya dakatar da mai rikon mukamin shugaban ma’aikata

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya dakatar da mai rikon mukamin shugaban ma’aikata kuma babban sakatare na Establishment Salisu Mustapha, bisa zargin zarge-zargen da ake yi na yanke albashin ma’aikatan gwamnatin Kano.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24 a ranar Alhamis, ya tabbatar da cewa an kuma umurci Salisu Mustapha da ya ajiye mukaminsa na babban Sakatare na Establishment, a karkashin ofishin shugaban ma’aikata, don ba da damar gudanar da bincike ba tare da tangarda ba.

InShot 20250115 195118875
Talla

Domin tabbatar da ci gaba da gudanar da harkokin mulki, gwamnan ya amince da nadin Malam Umar Muhammad Jalo, Babban Sakatare na REPA, a matsayin sabon shugaban ma’aikata na riko, har sai an kammala binciken da ake yi.

Gwamna Yusuf ya sake jaddada matsayinsa na kin amincewa da almundahanar kudi, yana mai gargadin cewa duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci mummunan hukunci.

Gwamnatin Kano ta bukaci Tinubu ya dauke Aminu Ado Bayero daga jihar

Kwamitin binciken da Abdulkadir Abdussalam ke jagoranta da aka kaddamar a yau, an ba shi wa’adin kwanaki bakwai don gano inda matsalar ta ke tare da gabatar da sakamakon binciken.

A farkon wannan watan ne aka nada Salisu Mustapha a matsayin shugaban ma’aikata na riko, biyo bayan hutun jinya da aka baiwa babban shugaban ma’aikatan, Abdullahi Musa, wanda yanzu haka yake jinya a kasar Indiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...