Gwamnatin Kano ta bukaci Tinubu ya dauke Aminu Ado Bayero daga jihar

Date:

Gwamnatin jihar kano ta bukaci shugaban kasa Bola Tinubu da ya dauke sarkin kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero daga jihar kano domin samar da masalaha a jihar, la’akari da yadda wasu ke amfani dawannan damar wajen neman tayar da husuma a fadin jihar .

 

Mataimakin gwamnan jihar kano kwamrat Aminu Abdussalam Gwarzo ne ya bayyana hakan, inda yace zaunar da sarkin kano na 15 a gidan sarkin na Nassarawa anyi shi da wata niya domin hana gwamnatin kano ta zauna lafiya da kuma kin yiwa al’ummar jihar abin da ya dace.

InShot 20250115 195118875
Talla

Freedom Radio ta rawaito kwamrat Aminu Abdussalam Gwarzo yace zanga-zanga da al’umma su ka fito a wannan satin, al’umma suna da hakkin fitowa domin nuna goyon bayan su kan abin da suke so.

Haka kuma suna da damar su nemi a cire sarkin kano na sha biyar daga gidan Nasarawa amma aka turo jami’an tsaro suka hana su tare da kama wasu daga cikinsu.

Gwamnan Kano ya kafa kwamiti domin bincikar dalilin yankewa ma’aikatan albashin

Gwarzo ya kuma ce suna kira ga shugaban kasa da ya gaggauta dauke sarkin kano na sha biyar daga cikin jihar Kano domin barin al’umma su zauna lafiya.

Gwamnatin kano ta ce yadda doka ta kawo tsohon sarkin haka doka ce ta kawo sabon sarkin dan haka abar doka ta yi aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...