Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja’atu Muhammad ta ce har yanzu tana nan akan bakarta kan maganar da ta fada akan mai baiwa shugaban kasa shawara akan harkokin tsaro Nuhu Ribado.

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito cewa Nuhu Ribado ya yi barazanar maka Hajiya Naja’atu Muhammad a kotu matukar bata janye kalaman da tayi a akansa ba.

Hajiya Naja’atu Muhammad ta bayyana hakan ne yayin wata hira da ta yi da gidan Rediyon Premier dake Kano.

InShot 20250115 195118875
Talla

“Ina nan akan bakara ba zan janye kalami na ba, ballantana na ba shi hakuri, idan ya so ya kaini Kotun koli”. Inji ta

Ta ce maganar da ta fada ba karya ba ce, sai dai idan shi ne ya yiwa mutane karya lokacin da ya ke a matsayin shugaban hukumar EFCC.

Idan za’a iya tunawa dai Hajiya Naja’atu Muhammad ta ce a lokacin da Nuhu Ribado yake a matsayin shugaban hukumar EFCC ya ce Tinubu cikakken dan cin hanci da rashawa ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...