APC ta kori tsohon ministan Buhari

Date:

Jam’iyyar APC ta kori tsohon gwamnan jihar Osun kuma tsohon ministan cikin gida Rauf Aregbesola, a kan zarginsa da yin abubuwan da suka saba wa jam’iyyar.

Reshen jam’iyyar na jihar ta Osun shi ne ya tabbatar da korar a wata wasika da ya fitar.

 

InShot 20250115 195118875
Talla

Aregbesola, wanda ya kasance ministan cikin gida a lokacin gwamnatin da ta gabata, ya jagoranci wani bangare na jam’iyyar ta APC a jihar, bangaren da aka yi wa lakabi da “The Osun Progressives,” wanda kuma daga baya aka sake masa lakabi da ”Omoluabi Caucus”.

Babban Dalilin da ya sa na Shiga Siyasa – Sani Danja

Korar tsohon gwamnan ta biyo bayan taron da bangaren da yake jagoranta ne wato Omoluabi Caucus, ya gudanar kuma karkashin jagorancin, Aregbesola.

A lokacin taron bangaren ya sanar da aniyarsa ta ficewa daga APC,inda ya bayar da hujjar raguwar tasirin jam’iyyar a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...