APC ta kori tsohon ministan Buhari

Date:

Jam’iyyar APC ta kori tsohon gwamnan jihar Osun kuma tsohon ministan cikin gida Rauf Aregbesola, a kan zarginsa da yin abubuwan da suka saba wa jam’iyyar.

Reshen jam’iyyar na jihar ta Osun shi ne ya tabbatar da korar a wata wasika da ya fitar.

 

InShot 20250115 195118875
Talla

Aregbesola, wanda ya kasance ministan cikin gida a lokacin gwamnatin da ta gabata, ya jagoranci wani bangare na jam’iyyar ta APC a jihar, bangaren da aka yi wa lakabi da “The Osun Progressives,” wanda kuma daga baya aka sake masa lakabi da ”Omoluabi Caucus”.

Babban Dalilin da ya sa na Shiga Siyasa – Sani Danja

Korar tsohon gwamnan ta biyo bayan taron da bangaren da yake jagoranta ne wato Omoluabi Caucus, ya gudanar kuma karkashin jagorancin, Aregbesola.

A lokacin taron bangaren ya sanar da aniyarsa ta ficewa daga APC,inda ya bayar da hujjar raguwar tasirin jam’iyyar a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya karya farashin man fetur

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Matatar mai ta Dangote ta karya...

Tallafawa al’umma: Kungiyar cigaban Unguwar Zango ta Karrama Dr. Muhammad Musa Zango

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Makaman Bichi Alhaji Isyaku Umar Tofa...

Babban Dalilin da ya sa na Shiga Siyasa – Sani Danja

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Mai baiwa gwamnan Kano shawara na...

Musa Iliyasu ya bayyana dalilin da yasa Kwankwaso ke neman komawa APC yanzu

Babban Daraktan kudi na hukumar raya kogunan Hadeja-Jama'are kuma...