Sani Danja ya hada kai da jami’ar KHAIRUN don inganta rayuwar matasan Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin jihar Kano ta yi alkawarin yakar shaye-shayen miyagun kwayoyi ta hanyar baiwa matasa ingantaccen ilimi.

Kadaura24 ta rawaito mai baiwa gwamnan jihar Kano shawara na musamman kan harkokin Matasa da wasanni Alhaji Sani Musa Danja ne ya bayyana hakan lokacin da ya ziyarci jami’ar Sheikh Isyaka Rabi’u KHAIRUN dake Kano.

“Al’amarin shaye-shayen miyagun kwayoyi da wasu daga cikin matasan mu suke yi, yana ci mana tuwo a kwarya hakan tasa muka ga dacewar mu zo domin kulla alakar da jami’ar KHAIRUN domin ganin sun cimma manufar gwamnatin mu ta samar da ilimi ga matasa”. Inji Sani Danja

InShot 20250115 195118875
Talla

” Samar da ilimi da kawar da shaye-shaye na daga cikin kudirin mai girma Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf domin ceto yara matasa daga harkar shaye shaye da zaman kashe wando”.

Tinubu ya ba da umarnin a baiwa Kwankwaso, Bichi da sauran wadanda ya nada takardun kama aiki

” mun San Wannan jami’ar mai zaman kanta ce , amma Muna so a samar da tsarin da zai saukakawa matasa don sun sami ingantaccen ilimi don kyautata rayuwarsu.

A nasa jawabin shugaban jami’ar KHAIRUN Prof. Abdulrashid Garba bayan nuna farin cikinsa ga ziyarar mashawarcin gwamnan kan harkokin Matasa da wasanni, ya kuma ba da tabbacin jami’ar KHAIRUN zata hada kai da ofishinsa Sani Danja don inganta rayuwar matasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...