Cigaban Kano: Murtala Sule Garo Ya Fadawa Ganduje da Kwankwaso Gaskiya

Date:

Tsohon Kwamishinan Kananan Hukumomin na jihar Kano kuma dan takarar mataimakin Gwamna a jam’iyyar APC a zaben shekarar 2023, Murtala Sule Garo ya bayyana damuwa kan rashin jituwa da ake samu tsakanin tsoffin gwamonin jihar da suka hada da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da Abdullahi Umar Ganduje.

Kwankwaso da Ganduje, waɗanda abokan siyasa ne a da, sun tsunduma cikin rikicin da ya ƙi ya ƙi cinye wa ton 2016.

Majalisar dokoki ta karbi korafi kan tsawaita wa’adin aiki ga shugaban ma’aikata da wasu da gwamnan Kano ya yi

Sai dai a yayin da ya ke jawabi a taron tsofaffin ƴan majalisar jiha na majalisa ta 8 da ta 9 na jihar Kano, Garo ya yi kira ga Ganduje da Kwankwaso su hada kai don ciyar da Kano gaba.

“Kira na shi ne bangaren Gwamonin mu, Abin takaici a jihar Kano, ka ga jiha irin jihar Zamfara wacce ta ke kanwa ce ta nesa ga Kano , tsoffin gwamnoninsu za ka ga an yi taro dukkan su sun zo , sun hadu duk da banbancin ra’ayi da na jam’iyya ,amma duk da haka su kan hadu su tattauna abinda zai ci da jiharsu gaba”.

Talla

“Amma mu a nan jihar Kano, abin mamaki shugabannin mu, iyayenmu tsofaffin Gwamnoni ba za su iya haduwa su tattauna abinda zai kawo ci gaba ga jihar Kano ba .

“A don haka mu na rokon su, mu na kira gare su da su hade kansu mu na yi musu addu’a, lallai su kawar da banbance- banbancen da ke tsakanin su indai da gaske su na son ci gaban Kano”,inji Garo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...