Cigaban Kano: Murtala Sule Garo Ya Fadawa Ganduje da Kwankwaso Gaskiya

Date:

Tsohon Kwamishinan Kananan Hukumomin na jihar Kano kuma dan takarar mataimakin Gwamna a jam’iyyar APC a zaben shekarar 2023, Murtala Sule Garo ya bayyana damuwa kan rashin jituwa da ake samu tsakanin tsoffin gwamonin jihar da suka hada da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da Abdullahi Umar Ganduje.

Kwankwaso da Ganduje, waɗanda abokan siyasa ne a da, sun tsunduma cikin rikicin da ya ƙi ya ƙi cinye wa ton 2016.

Majalisar dokoki ta karbi korafi kan tsawaita wa’adin aiki ga shugaban ma’aikata da wasu da gwamnan Kano ya yi

Sai dai a yayin da ya ke jawabi a taron tsofaffin ƴan majalisar jiha na majalisa ta 8 da ta 9 na jihar Kano, Garo ya yi kira ga Ganduje da Kwankwaso su hada kai don ciyar da Kano gaba.

“Kira na shi ne bangaren Gwamonin mu, Abin takaici a jihar Kano, ka ga jiha irin jihar Zamfara wacce ta ke kanwa ce ta nesa ga Kano , tsoffin gwamnoninsu za ka ga an yi taro dukkan su sun zo , sun hadu duk da banbancin ra’ayi da na jam’iyya ,amma duk da haka su kan hadu su tattauna abinda zai ci da jiharsu gaba”.

Talla

“Amma mu a nan jihar Kano, abin mamaki shugabannin mu, iyayenmu tsofaffin Gwamnoni ba za su iya haduwa su tattauna abinda zai kawo ci gaba ga jihar Kano ba .

“A don haka mu na rokon su, mu na kira gare su da su hade kansu mu na yi musu addu’a, lallai su kawar da banbance- banbancen da ke tsakanin su indai da gaske su na son ci gaban Kano”,inji Garo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...