Gobara ta yi barna a Jami’ar KUST ta Wudil Dake Kano

Date:

Daga Nura Abubakar
Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce ta kashe gobarar da ta kone ofisoshi guda biyar, a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Kano dake Wudil (KUST) a Kano.
 Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Alhaji Saminu Abdullahi ya raba wa manema labarai ranar Lahadi a Kano.
 “Mun samu kira a sashin mu na Wudil daga jami’an tsaro da misalin karfe 12:04 na safe cewa gobara ta tashi a wani benen Jami’ar.
 Bayan samun labarin, mun aika da motar kashe gobara zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 12:07 na safe, domin shawo kan lamarin,” in ji sanarwar.
 Abdullahi ya bayyana cewa gobarar ta kone dukkan ofisoshin guda biyar gaba daya.
 Ya kara da cewa wutar lantarki ce ta haddasa gobarar.
 Ya bukaci jama’a da su kara yin taka-tsan-tsan da kuma daukar matakan kariya domin gudun tashin gobara Musamman a Wannan Lokaci da sanyi yake kara kamari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Nasarar da Ɗaliban Kano suka Samu a NECO Kokari ne na Gwamnatin Ganduje – Sanusi Kiru

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Muhammad Sanusi...

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa...

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...

Kungiyar Karamci United Family ta Karrama Shugaban gidan Radiyon Pyramid Saboda Taimakawa Al’umma

Shugaban gidan Radio tarayya Pyramid FM Dr. Garba Ubale...