Abubakar Sabo na Dala Radio ya sami Sabon Mukami

Date:

Sabon shugaban riko na kungiyar daliban Hausa a kwalejin ilmi ta Aminu Kano AKCOE take da hadin gwiwa da jami’ar tarayya da ke Dustin-ma a jihar Katsina FUDMA kuma na farko a tarihin makarantar kwamared Abubakar Sabo ya ba da tabbacin yin aiki tukuru, tare da dukkannin shugabannin kungiyar, domin samar da duk wani cigaba a tafiyar kungiyar.

Ya kuma nemi hadin kan sauran wadanda suka nemi takara amma ba su sami nasara ba dama ragowar daliban makarantar na sashin Hausa, da su ba da hadin kai wajan cigaban kungiyar domin ciyar da ita gaba, da Kuma ganin kara bunkasar harshen na Hausa a fadin Duniya.

Talla

A jawaban su daban-daban shugaban kwamitin samar da kungiyar tare tabbatuwar shugabannin rikon dakta Magaji Ahmad Gaya da sakataren sa malam Ahmad Mikha’il sun ja hankalin sabbin shugabannin rikon da su zama masu juriya da hakuri tare da gaskiya da rikon Amana don samar da cigaban kungiyar wajan ganin ta je duk in da ya kamata ta je.

An dai nada Abubakar Sabo a matsayin shugaba sai Rabi Ahmad mataimakiyar shugaba da Abdulmusawwir a matsayin magatakarda da sauran mutane goma sha biyu, a mukamai daban-daban.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...