Jarumin Izzar so Lawan Ahmad ya Roki Kudi Wajen Masoyansa

Date:

Daga Habiba Bukar Hotoro

 

Fitaccen jaruman masana’atar kannywood Lawal Ahmad wanda kuma shine babban jarumin shirin mai dogon zango na Izzar ya riko al’umma Musamman masoyansa dasu taimaka Masa da kudi.

Kadaura24 ta rawaito Lawan Ahmad yayi rokon ne a Shafin sa na Facebook Inda ya rubuta Cewa yana son yaci albarbacin fiyayyen halitta annabi Muhammad S A W, Sannan yasa Lambar asusunsa.

Nima yau inason cin albarkacin Annabi Muhammad s.a.w Ga account number 2119215122 UBA Bank Nagode“.

Bayan Sanya Wannan bayani ne ba’afi awa daya ba sai Ahmad Lawan din ya Fara sanya bayanan kudaden da masoyansa Suka tura masa a cikin Asusun bunkinsa.

Daga bisani dai jarumin ya wallafa Wani video Wanda ya fito a ciki yana Mika godiyar sa ga Waɗanda Suka tura masa kudin tare da yi musu addu’ar fatan alkhairi.

A Jiya Laraba dai Wani mawaki Daga kudancin Kasar nan mai Suna Dovido ya rokin Yan Uwa da abokan arzikin sa ru tura masa kudi, Kuma suka tura Masa Inda a yini Guda ya hada Naira Miliyan 114.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...