Kungiyar Dillalan Man Fetur Ta Nigeriya ta Cimma Matsaya da Matatar Mai ta Ɗangote

Date:

Ƙungiyar Dilallan Man Fetur ta Najeriya (IPMAN), ta cimma yarjejeniya da Matatar Dangote kan fara dakon man fetur kai-tsaye daga wajen su.

Yarjejeniyar ta samu ne bayan makonni da aka ɗauka ana tattaunawa tsakanin ɓangarorin biyu kan samar da man fetur a sauƙaƙe kuma a farashi mai rahusa.

Da yake magana da manema labarai a Abuja, Shugaban IPMAN, Abubakar Garima, ya ce yarjejeniyar za ta inganta haɗin gwiwa tsakaninsu, wanda zai taimaka wajen samar da isasshen man fetur mai rahusa a faɗin ƙasar.

Talla

Garima, ya yi kira ga mambobin IPMAN da su bai wa matatar Dangote goyon baya domin bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa.

“Bayan ganawa da Aliko Dangote da mahukuntansa a Legas, muna farin cikin sanar da cewa Matatar Dangote za ta samar wa IPMAN da man fetur, dizal, da kalanzir kai-tsaye don rabawa zuwa manyan rumbunan ajiyarmu da wuraren sayarwa,” in ji shi.

Gwamnan Kano zai Aurar da ‘yar Kwakwaso ga dan Mangal

Ya kuma shawarci mambobin IPMAN da su dogara da Matatar Dangote da matatun man Najeriya, wanda zai ƙara samar da ayyukan yi da kuma tallafa wa manufofin cigaba na Shugaba Bola Tinubu.

Tun da farko a watan Nuwamba, IPMAN ta bayyana cewa tsadar jigilar mai daga Matatar Dangote ta sa wasu dilallai neman mai rahusa.

Rashin cimma yarjejeniya tsakanin IPMAN da Dangote ya janyo tsaiko da ƙalubale wajen samar da man fetur a baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...