Da Gawuna aka baiwa kujerata ta Minista da ban damu ba – T Gwarzo

Date:

Tsohon ƙaramin ministan gidaje na Najeriya, Abdullahi Tijjani Gwarzo ya ce ya yi mamakin sauke shi da a aka yi daga muƙaminsa.

Yayin wata hira da BBC kwanaki bayan sauke shi , T Gwarzo ya ce babu wani laifi da ya yi, wanda ya janyo aka sauke shi daga muƙamin nasa, sabod a cewarsa ya yi iya baƙin ƙoƙarinsa a muƙamin da aka ba shi.

Talla

”Batun ya zo min da mamaki, domin ba na tunanin wani abu mai kama da wannan zai faru da ni”, in ji shi.

Ya ƙara da cewa Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi la’akari da tarayyarsu tun ta da can wajen naɗa shi muƙamin.

Gwamnan Kano zai sauya wasu daga cikin kwamishinoninsa

Ya ce fiye da shekara 14 suna tare da Tinubu tun a jam’iyyar ACN, shi da Nuhu Ribadu da Sanata George Akuwam – da ke riƙe da muƙamin sakataren gwamnati a yanzu.

Sai dai ya ce Allah ne ke ba da mulki, kuma ya karɓe a duk lokacin da ya so, don haka ya ce yana gode wa shugaban ƙasar, bisa damar da ya ba shi a gwamnatin tasa.

Ya ce kamata yayi ace da aka cire shi a baiwa wanda ya yiwa jam’iyyar APC takarar gwamnan jihar kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, indai batu ake na Kano ta tsakiya.

 

“Amma wanda aka baiwa kujerar bani da wata matsala da shi, kuma Ina yi masa fatan alkhairi, amma wadanda suka kitsa cire ni sun yi maganar siyasa ne”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...