Fadar Shugaban Kasa ta bayyana dalilin da yasa Tinubu bai cire matawalle ba

Date:

Bayo Onanuga, mai ba da shawara na musamman kan yada labarai ga Shugaba Bola Tinubu, ya ce zarge-zargen da suka danganta Bello Matawalle da hannu a ayyukan ‘yan fashin daji a yankin arewa maso yamma sun bayyana ba gaskiya ba ne.

Matawalle shi ne karamin ministan tsaro. An bar shi a ofis yayin da Tinubu ya yi garambawul ga majalisar ministocinsa a ranar 23 ga Oktoba.

Talla

TheCable ta rawaito cewa yayin da ya ke magana a wata hira da Arise TV a ranar Laraba, Onanuga ya ce ba a kori Matawalle, tsohon gwamnan Zamfara, ba saboda ofishin mai ba bawa shugaban kasa shawara kan tsaro ya binciki zarge-zargen da suka shafi alakarsa da ‘yan fashin daji kuma suka gano ba su da tushe.

 

Onanuga ya ce zarge-zargen da ake yi wa Matawalle “kawai ƙirƙira ne” kuma suna da alaka da siyasa.

Cire T-Gwarzo daga Minista: Bashir Gentile ya aikawa Tinubu Sako

“Gwargwadon abin da na sani, yawancin waɗannan abubuwan zarge-zarge ne kawai,” in ji mai taimaka wa shugaban ƙasar.

“A cikin ɗayansu, na samu wani abu makamancin haka na aika wa Ribadu na tambaye su: ‘Kun ji labarin wannan?’

“Mai bai wa shugaban kasa shawara ya ce: ‘A’a. Mun binciki yawancin waɗannan abubuwan; ba gaskiya bane’. Mutane dai suna fitowa da nau’ikan abubuwan ƙarya da zarge-zarge. Shi ya sa mutumin (Matawalle) har yanzu yana cikin majalisar ministocin.

Talla

“Shugaban ƙasa, ina da tabbacin, ya ji labarai da dama game da shi. Domin yana nan a wurin ya nuna cewa… kamar yadda na faɗa, an binciki wasu daga cikin waɗannan abubuwan; an gano ba gaskiya ba ne.

“Ofishin NSA ya riga ya binciki wasu daga cikin waɗannan zarge-zargen. Kawai ƙirƙira ne.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...

Zargin kwace gona: Majalisar Dokokin Kano zata binciki Shugabar Karamar Hukumar Tudun Wada (ALGON)

    Majalisar dokokin jihar Kano, ta sha alwashin gudanar da...