Cigaban ilimi: An bude makarantu uku da Rarara ya gina

Date:

 

Shahararren mawakin siyasar Nan Alhaji Dauda Kahutu Rarara ya jagoranci bude wasu makarantun Firamare guda uku da ya Gina da kuɗinsa a wasu kauyukan jihar Katsina.

Mawakin ya dai gina makarantar ne daya a Unguwar Da’iya Kahutu sai guda a Gidan Dari da kuma Barmi dukkanin su a karamar hukumar Dan ja dake jihar Katsina.

Da yake jawabi a wajen taron bude makarantun Alhaji Dauda Kahutu Rarara ya ce ba samar da makarantun ne saboda taimakawa al’ummar yankin da su sami nagartaccen Ilimi saboda shi ne gishirin Rayuwa al’umma.

Talla

” Na samar muku da wadanda makarantun ne da kudin aljihunna, don haka ina fatan iyayen yara za su nuna farin cikinsu ta hanyar tura yaransu makarantun tare da Kula da makarantun don su jima ana amfanarsu”. Inji Rarara

Da dumi-dumi: Jarumi Adam A Zango ya sami Mukami

A wata sanarwa da hadimin Rarara kan harkokin yada labarai Rabi’u Garba Gaya ya fitar, ya ce Rarara ya kuma dauki nauyin malaman makaranta 300 domin baiwa daliban ingantaccen Ilimi.

“Malaman za mu rabasu zuwa makarantun guda uku kuma za mu rika biyansu duk wata ka ga suma sun sami aikin yi, Sannan Muna kira a garesu da su zamu masu mai da hankali wajen yin aikin da aka dauke su”. A cewar Rarara

Talla

Alhaji Dauda Kahutu Rarara ya kuma ba da tabbacin zai cigaba da gudanar da aiyukan da zasu inganta rayuwar al’umma, don inganta rayuwar yara masu tasowa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...