Da dumi-dumi: Jarumi Adam A Zango ya sami Mukami

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gidan Talabijin na Qausain TV ya nada fitaccen jarumin fina-finan Kannywood kuma mawaki Adam A. Zango a matsayin Darakta Janar na gidan Talabijin.

Shugaban kamfanin Qausain, Alh Nasir Idris ne ya bayyana hakan, a wata sanarwa a ranar Litinin a Abuja, ya bayyana cewa nadin Mista Zango a matsayin Darakta Janar din ya fara aiki nan take.

A cewar sanarwar, an amince da nadin ne yayin wani taron hukumar daraktocin kamfanin.

Dalilai 2 da suka sa Gwamnatin Kwankwasiyya ta ce ta cire Sarki Aminu Bayero – Jafar Sani Bello

Alhaji Idris ya kara da cewa an nada tsohon Gwamnan Soja na Jihar Kano, Kanar Sani Bello (mai ritaya) a matsayin Shugaban Hukumar daraktocin kamfaninm

“Nadin Bello a matsayin Shugaban hukumar daraktocin kamfanin na tsawon shekaru hudu ne, kamar yadda dokar Kamfanoni ta tanada.

Talla

Idris ya ce an nada tsohon ministan sadarwa Farfesa Isa Pantami a matsayin mai sanya idanu kan harkokin shugabannin kamfanin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...