Cigaban ilimi: An bude makarantu uku da Rarara ya gina

Date:

 

Shahararren mawakin siyasar Nan Alhaji Dauda Kahutu Rarara ya jagoranci bude wasu makarantun Firamare guda uku da ya Gina da kuɗinsa a wasu kauyukan jihar Katsina.

Mawakin ya dai gina makarantar ne daya a Unguwar Da’iya Kahutu sai guda a Gidan Dari da kuma Barmi dukkanin su a karamar hukumar Dan ja dake jihar Katsina.

Da yake jawabi a wajen taron bude makarantun Alhaji Dauda Kahutu Rarara ya ce ba samar da makarantun ne saboda taimakawa al’ummar yankin da su sami nagartaccen Ilimi saboda shi ne gishirin Rayuwa al’umma.

Talla

” Na samar muku da wadanda makarantun ne da kudin aljihunna, don haka ina fatan iyayen yara za su nuna farin cikinsu ta hanyar tura yaransu makarantun tare da Kula da makarantun don su jima ana amfanarsu”. Inji Rarara

Da dumi-dumi: Jarumi Adam A Zango ya sami Mukami

A wata sanarwa da hadimin Rarara kan harkokin yada labarai Rabi’u Garba Gaya ya fitar, ya ce Rarara ya kuma dauki nauyin malaman makaranta 300 domin baiwa daliban ingantaccen Ilimi.

“Malaman za mu rabasu zuwa makarantun guda uku kuma za mu rika biyansu duk wata ka ga suma sun sami aikin yi, Sannan Muna kira a garesu da su zamu masu mai da hankali wajen yin aikin da aka dauke su”. A cewar Rarara

Talla

Alhaji Dauda Kahutu Rarara ya kuma ba da tabbacin zai cigaba da gudanar da aiyukan da zasu inganta rayuwar al’umma, don inganta rayuwar yara masu tasowa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...