Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado ya kai ziyarar jajantawa Yan kasuwar Kantin Jim kadan da dawowarsa daga ziyarar aiki da ya je Abuja.
A wata sanarwa da sakataren yada labaran sarkin Abubakar Balarabe kofar Na’isa ya aikowa kadaura24, ya ce dubun dubatar masoya da magoya baya ne suka yi cincirundo domin raka mai Martaba Sarkin kasuwar ta Kantin kwari.

Da yake jajantawa wadanda suka gamu da ibtila’in gobarar, Sakin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yayi addu’ar Allah ya mayar da asarar da akayi a kasuwar tareda addu’ar Allah ya kiyaye afkuwar hakan anan gaba.
A 2027 za mu sallami Kwankwaso daga Siyasa – Doguwa
Alhaji Aminu Ado Bayero ya kuma godewa Jami’an Hukumar kashe gobara ta jihar Kano da Jami’an tsaro da Kungiyar Yan kasuwar da dai daikun al’uma bisa yadda suka bada dugunmawa wajan tabbatar da kashe gobarar.
Sarkin daga nan sai ya bukaci Yan kasuwa da sauran al’umma su cigaba da yin Addu’o’i domin kiyayewar afkuwar irin wannan ibtila’i tare da neman samun sassaucin al’amura na rayuwar yau da kullum.

Mai Martaba Sarkin na Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya kai ziyarar aiki ne babban Birnin Tarayya Abuja tare da halartar wasu tarurruka, inda daga dawowar sa ne ya zarce domin yin jaje ga Yan kasuwar.