An janye yan sandan da suka mamaye sakatariyar kananan hukumomin jihar Rivers

Date:

Sufeto-Janar na ƴan sanda ya bada umarnin janye jami’an ƴan sanda da su ka mamaye sakatariyar ƙananan hukumomi a Rivers na tsawon watanni uku.

Talla

An mamaye sakatariyar ne a watan Yuni sakamakon rashin jituwar da aka samu tsakanin shugabannin kwamitin riko da ke goyon bayan Gwamna Siminalayi Fubara da kuma shugabannin kananan hukumomi da suka sauka, wadanda suka kasance masu biyayya ga Nyesom Wike, Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT).

Talla

Daily Trust ta rawaito cewa sai dai a yau Litinin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ƴansanda a jihar Rivers, SP Grace Iringe-Koko, ya ce sabon kwamishinan yansandan jihar, CP Bala Mustapha, ya mika umarnin babban sufeton ‘yan sanda, IGP Kayode Egbetokun. domin a janye dukkan jami’an da aka tura a baya don rufe sakatariyar da kuma tsare ta.

Ya ce umarnin janye ƴansandan na nan take ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abin mamaki: Barawo ya sace Motar dake cikin ayarin motocin gidan gwamnatin Kano

Wani barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin jihar...

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...