Rashin Cika alkawari: An gurfanar da Hafsat Idris ta Kannywood a gaban kotu

Date:

Daga Habiba Bukar Hotoro
Kamfanin shirya fina-finai na Uk entertainment ya maka fitacciyar jarumar Kannywood, Hafsat Idris wadda akewa lakabi da Barauniya a gaban kotu bisa zargin Saba alkawarin da Suka kulla fa Kamfanin.
 A karar da Kamfanin ya shigar gaban babbar kotun Kano Mai lamba 14 da ke zamanta a karamar hukumar Ungogo, an zarge jarumar da karbar Naira miliyan 1.3 domin ta fito a cikin wani Shiri Mai Dogon zango amma ta gagara cika alkawarin yin aikin Kamar yadda aka kulla yarjejeniyar da ita kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.
 Mai shigar da karar ya ce kamfanin yayi asara Mai yawa saboda karya alkawarin da Hafsat Idris ta yi.
 Kamfanin shirya fina-finan ya bukaci kotu ta Umarci Hafsat Idris ta bayar da Naira miliyan 10 a matsayin diyyar asarar data jawowo musu.
 Wadda ake tuhuma, ta hannun lauyanta, ta gabatar da martani na musamman kan da’awar.
 Kotun ta dage sauraren karar.
 Wacece Hafsat Idris?
 Hafsat Ahmad Idris (an haife ta 14 Yuli 1987) yar wasan fina-finan Kannywood ce a Najeria.
 Ta fito a fim dinta na farko mai suna Barauniya a Shekarar (2016).
 Ta Jarumar Shekara 2019 a Cikin takwarorinta Mata dake a masana’antar Kanywood.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...