Kotu ta tusa keyar alƙalin bogi zuwa gidan yari a Kano

Date:

Wata kotun Musulunci ta tisa ƙeyar wani alƙalin bogi zuwa gidan yari a Jihar Kano.

Dubun alƙalin bogin ta cika ne bayan da ya gabatar da kansa a matsayin alkali daga Jihar Jigawa a gaban Kotun Musulunci da ke unguwar Kurma, Ƙaramar Hukumar Fagge.

Yan arewa ku yi mana aikin gafara, mun gaza kare ku – ACF

Asirin alƙalin bogin ya tonu ne a lokacin da ya je kotun neman belin wasu mutane biyu wadanda ake zargi da laifin damfara da cin amana.

Kotun ta amince da ba shi belin mutanen ne a bisa sharaɗin sai ya kai jami’an kotu gidansa, amma nan take ya ƙi amincewa.

 

Da aka tsananta bincike daga baya sai aka gano cewa ungulu da kan zabi ya yi, ma’aikacin shari’a ne, amma bai taɓa zama alkali ba.

Kungiyar Samarin Tijjaniyya sun Allah wadai da kara kudin man fetur a Nigeria

A lokacin da aka gurfanar da shi, ya amsa laifinsa, sannan ya roki alkali ya yi masa sassauci.

Khadi Umar Lawan Abubakar ya ba da umarnin tsare shi a gidan yari zuwa ranar 23 ga watan Satumba, 2024 domin ci gaba da shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...