‘Yan arewa ku yi mana aikin gafara, mun gaza kare ku – ACF

Date:

 

Shugaban majalisar gudanarwar Kungiyar tuntuba ta arewacin Najeriya wato ACF, Alhaji Bashir Dalhatu ya nemi gafarar ‘yan arewacin kasar saboda abinda ya kira gazawar su wajen kare yankin daga fadawa rikici mafi muni a tarihinsa.

 

Dalhatu ya ce suna ci gaba da lalubo hanyar shawo kan Waɗannan matsaloli da suka yiwa yankin kamun kazar kuku.

Karin Farashin Mai: Ya kamata yan majalisu su takawa NNPC burki – Gidauniyar GCAF

Shugaban ya ce yankin arewacin kasar zai rungumi shirin sake fasalin kundin tsarin mulki da jagorancin Najeriya domin ci gaba da kare darajar da martabar yankin.

A jiya laraba ne dai wasu daga cikin shugabannin yankin suka gudanar da mahawara a kan matsalolin da suka addabi yankin.

Kungiyar Samarin Tijjaniyya sun Allah wadai da kara kudin man fetur a Nigeria

Cikin masu halartar taron harda tsohon Sakataren gwamnati Yayale Ahmed da Janar Halilu Akilu da Janar Muhammad Magoro da Tsohon Sufeto Janar MD Abubakar da tsoffin sakatarorin gwamnati Babacir Lawal da Boss Mustapha da kuma tsofin gwamnoni irin su Sule lamido da Adamu Muazu da Ibrahim Shekarau da Ali Sa’ad Birnin Kudu dai sauransu.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...