Karin kudin mai: Kayan masarufi kan iya tashi – kungiyar masu masana’antu

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Kungiyar masu masana’antu ta Najeriya MAN, ta ce karin kudin man fetur da aka yi zai iya haddasa tashin farashin kayayyaki a kasar.

Cikin wata sanarwa da Shugaban kungiyar ta MAN Segun Ajayi-Kadir ya fitar a ranar Laraba ta ce matakin zai iya shafar kudaden shigar jama’a.

Ajayi-Kadir na mayar da martani ne kan karin farashin man fetur da aka yi a kasar a ranar Talata.

Karin Farashin Mai: Ya kamata yan majalisu su takawa NNPC burki – Gidauniyar GCAF

Kamfanin NNPC ya kara farashin litar mai daga naira 568 zuwa naira 855, matakin da ya haifar da ce-ce-ku-ce a sassan Najeriya wacce ta dogara da mai a matsayin babbar hanyar samun kudaden shigarta.

“Yayin da farashin mai ya tashi, kudaden da mutane ke kashewa zai karu a fannonin sufuri da makamashi, wanda hakan zai rage kudaden da suke samu.” Ajayi-Kadir ya ce a cikin sanarwar kamar yadda rahotanni suka nuna.

2027: Atiku Obi da Kwankwaso sun fara tattaunawa – PDP

Ya kara da cewa lamarin zai fi shafar kananan masana’antu saboda kudaden da suke juya wa ba su taka kara sun karya ba.

Ko da yake, Shugaban na MAN ya ce bai yi mamaki da karin kudin litar man ba, duba da cewa farashin mai ya tashi a kasuwar duniya.

“Farashin mai ya tashi a duniya. Matatun manmu ba sa aiki kuma muna shigo da mai ne.” Ajayi-Kadir ya kara da cewa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...