Gwamnatin Kano za ta rika samar da Naira biliyan daya a duk shekara daga bangaren ma’adinai

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Gwamnatin jihar Kano na shirin inganta kudaden shigarta duk shekara da akalla Naira Biliyan daya daga ayyukan hakar ma’adanai a jihar.

Kwamishinan ma’aikatar ma’adanai da albarkatun kasa, Alhaji Safiyanu Hamza Kachako ne ya bayyana hakan a yau a wani shiri na rediyo kai tsaye da daraktan wayar da al’umma na ma’aikatar Adamu Ibrahim Dabo ya saurara kuma ya aikowa kadaura24 .

Alhaji Safiyanu Hamza Kachako ya bayyana cewa tun daga kafa ma’aikatar da Gwamnan Jihar Alhaji Abba Kabir Yusuf ya Yi, da kuma wa’adin da aka ba ta, ya zuwa yanzu tsare-tsare sun nisa na hada hannu da masu ruwa da tsaki a harkar daga ciki da wajen kasar nan don inganta tattalin arzikin jihar ta fuskanta hadar ma’adainai.

Sabuwar Badakala a Kano: An kama Kantomomi 3 da wasu 19, An kuma Saki Dan Kwankwaso

Kwamishinan ya kara da cewa ma’aikatar karkashin jagorancinsa ta tsara wani shiri na musamman wanda zai inganta kokarin gwamnati na samar da karin ayyuka da guraben aikin yi ga matasanmu masu tarin yawa da kuma kariya ga masu hakar ma’adinai masu lasisi da al’ummomin da ake aikin a inda suke da dai sauransu.

Talla
Talla

A cewarsa, za a iya cimma hakan ne ta hanyar ci gaba da tantance tasirin muhalli daga ma’aikatar tare da tabbatar da cewa kamfanonin hakar ma’adai suna tallafawa al’ummar da suke aiki a cikin su a duk inda suke a cikin jihar.

Kwamishinan ya kara da cewa a halin yanzu ma’aikatar tana yi lasisin hadar ma’adanai a Gidan Murtala dake birnin Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...