Yaki da Almubazzaranci da dukiyar al’umma: ICPC ta shirya wa yan jaridun yanar gizo bita a Kano

Date:

Shugaban Hukumar hana almubazzaranci da dukiyoyin al’ummar da sauran Laifuka ta kasa (ICPC) Dr Musa Adamu Aliyu ya shawarci ‘yan jarida da ke Kano da su rika mai da hankali wajen yin rahotanni da za su bunkasa tattalin arziki da inganta rayuwar al’umma.

Musa Aliyu ya bayyana haka ne a yayin wani horo na yini guda da aka shiryawa yan jaridun da ke yada labarai ta yanar gizo a karkashin kungiyarsa ta ASKOJ a Kano.

Ya ce idan aka yi la’akari da abubuwan da suka faru a kasar nan akwai bukatar ‘yan jarida su rika ba da labarin abubuwan ci gaba da za su daukaka martabar kasar a duniya, maimakon bayar da rahoton ayyukan tada kayar baya da sauran abubuwan da ba su dace ba.

Badakalar magunguna: Abubunwan da muka gano bayan kama Dan Kwankwaso da wasu mutum 4 – Muhuyi Magaji

Shugaban hukumar wanda ya samu wakilcin mataimakin kwamishinan ICPC Hassan Salihu, ya ce hukumar ta ga ya zama dole ta hada kai da dan jaridun yanar gizo domin su san abubuwan da ake bukata na bayar da rahoton ayyukan ICPC .

Ya kuma bukaci yan jaridan da su rika kiyaye ka’idoji da dokokin aikin jarida a koda yaushe, kuma su kaucewa yada labarai karya tare da yin Adalci a cikin rahotonninsu domin cigaban kasa.

Shugaban ICPC ya bayyana cewa, kyakkyawar alakar da ke tsakanin dan jaridar ta yanar gizo da hukumar abin a yaba ne, don haka ya kamata a kara himma wajen dorewarta domin ciyar da Nigeria gaba.

A nasa jawabin shugaban kungiyar ‘yan jaridu yanar gizo Yakubu Salisu ya yabawa hukumar ta ICPC bisa shirya wannan bita ta kwana daya ga yan jaridun dake aiki a yanar gizo.

Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya cika shekaru 63 a duniya

Ya bayyana cewa an kafa kungiyar ne a shekarar 2020 da nufin hada kan ‘yan jaridan domin cimma manufofin da aka sa gaba.

Yakubu Salisu ya bukaci mahalarta taron da su yi amfani da damar da suka samu domin bunkasa aikinsu a yada labarai.

A yayin horon an gabatar da kasidu daban-daban da suka shafi aikin hukumar.

Taron ya samu halartar masu jaridun yanar gizo daban-daban a Kano

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...