Iftila’i: Makaranta Ta Rushe Da Dalibai Suna Zana Jarabawa

Date:

 

Ginin makarantar sakandaren Kent Academy ya rushe da dalibansa a yayin da suke rubuta jarabawa a garin Jos na Jihar Filato.

A halin da ake ciki dalibai da dama sun makale a cikin baraguzan ginin makarantar mai hawa biyu da ke unguwar Busa Buji a Karamar Hukumar Jos ta Arewa.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 11 na safiyar ranar Juma’a 12 ga watan Yuli, 2024.

Talla

Tuni jami’an tsaro da jami’an gwamnati da al’ummar gari suka isa wurin inda suka dukufa gudanar da aikin ceto daliban da abin ya ritsa da su.

Da dumi-dumi: Doguwa Ya Fice Daga Jam’iyyar APC

Wakilin daily trust ya bayyana cewa an samu nasarar zakulo wasu daga cikin daliban, inda aka garzaya da wadanda suka samu rauni zuwa asibiti.

Ana kuma farganar samu asarar rai, amma ba a kai ga gano adadin ba, ko aka sanar a hukumance.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...