NDLEA Za Ta Sanya Kyamara A Jikin Jami’anta

Date:

Hukumar yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyi (NDLEA) za ta fara sanya kyamarori a jikin jami’anta domin inganta aikinsu.

Shugaban hukumar, Mohamed Buba Marwa, ya bayyana haka ne a wani taro a Abuja inda aka yi wa wasu jami’ai karin girma a ranar Laraba.

Talla

Marwa ya ce, “Za mu sa kyamarori a jikin jami’anmu a lokacin gudanar da muhimman ayyuka don tabbatar da amincinsu da kuma ingancin ayyukan.”

Rikicin Masarautun Kano: Yadda Matasa suka hana wakilin Sarki Sanusi shiga gidan sarkin Rano

Don kara inganta aikin hukumar, Marwa ya bayyana cewa NDLEA na kafa rassa biyar a Legas da Abuja.

Hukumar ta kara wa jami’anta 5,042 girma, ciki har da manyan hafsoshi biyu zuwa mukamin mataimakin kwamanda-janar.

Marwa ya ce karin girma ya biyo bayan tsauraran gwaje-gwaje da aka yi wa jami’an, yana mai bayar da tabbacin inganta yanayin aikin jami’an hukumar.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...