Kotu ta sanya ranar da Ganduje da Matarsa zasu bayyana a gabanta

Date:

Ana sa ran Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje da matarsa Hafsat da wasu mutum shida za su bayyana a gaban kotu a Jihar Kano.

Ana sa ran za su bayyana a gaban kotun da ke tuhumarsu da almundahana a ranar Alhamis.

Ana zarginsu da cin hanci da almundahanar biliyoyin kuɗaɗe.

Gwamnatin Jihar Kano ta NNPP ce, ta shigar da su ƙara a gaban Mai Shari’a Amina Adamu Aliyu.

Talla

A ranar 5 ga watan Yuni, kotu ta bai wa masu gabatar da ƙara izinin aike wa da waɗanda ake ƙara sammaci ta hanyar tallace-tallace ko jaridu, wanda kuma tuni aka wallafa a ranar 6 ga Yuni a jaridun Daily Trust da The Nation.

Abubunwan da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi

Waɗanda ake ƙara su ne Abdullahi Umar Ganduje, matarsa Hafsat, Abubakar Bawuro, Umar Abdullahi Umar, Jibrilla Muhammad, kamfanin Lamash Properties Limited, Safari Textiles Ltd, da Lesage General Enterprises.

A zaman kotun da ya gabata, lauya mai kare wadanda ake tuhuma na shida, Nuraini Jimoh SAN, kaɗai ne ya halarci zaman kotun.

Sauran waɗanda ake ƙara, ciki har da Ganduje, ba su aike da wakilci ba.

Mai Shari’a Amina Adamu ta sanya ranar 11 ga watan Yuli domin ci gaba da shari’ar.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...