Mun dauki matakan shawo kan matsalar mai a Nigeria – NNPC

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL, ya ce ya shawo kan matsalar da ta jawo dogayen layuka a gidajen mai da ke faɗin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin yau Alhamis, NNPCL ya ce an samu matsalar ne saboda “ɗawainiyar wajen jigilar man”.

“NNPCL na tabbatar da cewa wahalar da ake sha wajen samun man fetur a wasu sassan Najeriya ta faru ne saboda matsalar da aka samu wajen jigilar man kuma yanzu an kawo ƙarshen ta,” in ji sanarwar.

Sanarwa ta Musamman Daga Hukumar Samar da Ruwan sha ta Jihar Kano

Kamfanin ya ƙara da cewa ba shi da niyyar sauya farashin man, wanda tuni ‘yan kasuwa suka ƙara farashinsa a jihohi.

Lita ɗaya ta man ta zarta N750 a Abuja babban birnin ƙasar.

Tun daga farkon makon nan aka fara ganin layuka a gidajen mai a Abuja, inda matsalar ta bazu zuwa jihohi daga baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...