Daga Halima M Abubakar
Kwamishinan lafiya na jihar Kano Dr. Aminu Ibrahim Tsanyawa ya ziyarci wurin adana magunguna na jihar Kaduna.
Wannan na kunshe ne Cikin Wata sanarwa da Jami’a hulda da Jama’a ta Ma’aikatar Lafiya ta jihar Kano Hadiza M Namadi ta aikowa Kadaura24.
Dokta Tsanyawa ya bayyana cewa ziyarar Wani kokari ne na kyautata dangantakar Aiki tsakanin su, Kamar yadda Shugabanin Hukumar kula da magunguna ta Jihar kaduna suka ziyarci Kano don koyon yadda Aikin Shirin asusun Samar da magunguna yake gudana da yadda ake gudanar da shi.
Sanarwar tace kwamishinan ya kara da cewa jihar Kano ta zamo zakara a Cikin takwarorinta jihohin Kasar nan Saboda yadda Hukumar kula da magunguna ta Jihar Kano take gudanar da Shirin yadda ya kamata.
Dokta Tsanyawa ya kuma bayyana cewa Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje yana ba da cikakken goyon baya ga shirin Asusun Samar da magunguna a jihar wanda shine dalilin da ya sa jihar Kano ke ɗaukar nauyin shirin DRF a Najeriya a matsayin cibiyar Shirin a Kasar nan.
Daga karshe ya ce Gwamnan Kano koyaushe yana jajircewa tare da saka jari mai yawa a fannonin kiwon lafiya domin inganta rayuwar al’ummar jihar Kano.
Yayin Ziyarar Kwamishina Dr. Aminu Ibrahim Tsanyawa na tare da Babban Darakta na Hukumar kula da Magunguna ta Jihar Kano Pharm. Hisham Imamudden.