Ramadan: Zamu Kashe Naira Miliyan 15 Wajen Ciyar da Masu Karamin Karfi – Kantoman Dawakin Tofa

Date:

Daga Musa Mudi Dawakin Tofa

 

Sabon Kantoman mulki na Karamar hukumar Dawakin Tofa Dr. Kabiru Ibrahim Danguguwa ya sha alwashin rabawa talakawanta abinci na sama da naira Miliyan goma sha biyar, a lokacin Azumin watan Ramadan.

Kantoman mulkin ya bayyana haka ne yayin da ya jagorancin taron rantsar da mataimakinsa Honarabul Surajo Ahmad Chedi da sakatarensa Nuhu Ibrahim da kuma kansilolinsa 14, a harabar sakatariyar karamar hukumar .

Matsalar Tsaro: Kwamishinan Yan Sandan Kano Ya Baiwa Manyan Jami’an Rundunar Umarni

Dr. Danguguwa ya ce suna sane da halin matsin rayuwa da al’umma ke ciki, a matsayin somin-ta6i, cikin goman farko na watan Azumin Ramadan, kwamitin rikon da yake jagoranta zai raba kayan abinci na sama da naira miliyan goma sha biyar, a mazabu 11 dake karamar hukumar Dawakin Tofa.

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Sa a Buɗe Iyakokin Najeriya Da Nijar

Dakta Kabiru Ibrahim Danguguwa ya kara da cewa gwamnatinsa zata hidimtawa al’umma matuka da baiwa fannin ilimi fifiko, da inganta fannin lafiya dana tsaro da tsaftar muhalli da kuma bujuro da wasu manufofi da tsare-tsare wandanda zasu inganta rayuwar al’ummar karamar hukumar Dawakin Tofa .

Ya kuma bukaci yan kwamitin rikon karamar hukumar da su bashi hadin kan da ya dace domin ciyar da karamar hukumar Dawakin Tofa gaba, Sanna ya bukaci suna al’ummar karamar hukumar dasu tallafa musu da addu’o’i don su sami damar sauke nauyin da gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya dora musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta ɗaure wani ɗan Tiktok mai wanka a tsakiyar titunan Kano

    Wata kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya...

Damuna: Mun shirya inganta wuraren tsayarwar motocinmu – Kungiyoyin Direbobin na Kano

Kungiyar matuka motocin kurkura ta jihar Kano da Kungiyar...

Rasuwar Aminu Ɗantata babban rashi ne ba ga Nigeria kadai ba – Mustapha Bakwana

Daga Zakaria Adam Jigirya   Tsohon Mai baiwa gwamnan Kano shawarawa...

Gwamnatin Kano ta yabawa Tinubu saboda gyarawa da bude NCC DIGITAL PARK

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin jihar Kano ta yabawa Gwamnatin...