Ramadan: Zamu Kashe Naira Miliyan 15 Wajen Ciyar da Masu Karamin Karfi – Kantoman Dawakin Tofa

Date:

Daga Musa Mudi Dawakin Tofa

 

Sabon Kantoman mulki na Karamar hukumar Dawakin Tofa Dr. Kabiru Ibrahim Danguguwa ya sha alwashin rabawa talakawanta abinci na sama da naira Miliyan goma sha biyar, a lokacin Azumin watan Ramadan.

Kantoman mulkin ya bayyana haka ne yayin da ya jagorancin taron rantsar da mataimakinsa Honarabul Surajo Ahmad Chedi da sakatarensa Nuhu Ibrahim da kuma kansilolinsa 14, a harabar sakatariyar karamar hukumar .

Matsalar Tsaro: Kwamishinan Yan Sandan Kano Ya Baiwa Manyan Jami’an Rundunar Umarni

Dr. Danguguwa ya ce suna sane da halin matsin rayuwa da al’umma ke ciki, a matsayin somin-ta6i, cikin goman farko na watan Azumin Ramadan, kwamitin rikon da yake jagoranta zai raba kayan abinci na sama da naira miliyan goma sha biyar, a mazabu 11 dake karamar hukumar Dawakin Tofa.

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Sa a Buɗe Iyakokin Najeriya Da Nijar

Dakta Kabiru Ibrahim Danguguwa ya kara da cewa gwamnatinsa zata hidimtawa al’umma matuka da baiwa fannin ilimi fifiko, da inganta fannin lafiya dana tsaro da tsaftar muhalli da kuma bujuro da wasu manufofi da tsare-tsare wandanda zasu inganta rayuwar al’ummar karamar hukumar Dawakin Tofa .

Ya kuma bukaci yan kwamitin rikon karamar hukumar da su bashi hadin kan da ya dace domin ciyar da karamar hukumar Dawakin Tofa gaba, Sanna ya bukaci suna al’ummar karamar hukumar dasu tallafa musu da addu’o’i don su sami damar sauke nauyin da gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya dora musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...