Zamu fi Baiwa Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Al’ummar Gwarzo Fifiko – Kantoman Gwarzo

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Kantoman karamar hukumar Gwarzo Dr.Mani TSoho ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa don tabbatar da zaman lafiya a karamar hukumar Gwarzo.

Dr.Mani Tsoho ya yi wannan alkawarin ne a lokacin rantsar da mataimakinsa, sakatare da kansilolin karamar hukumar a cibiyar Addinin Musulunci ta Gwarzo .

“Muna fuskantar kwararowar masu garkuwa da mutane da ‘yan fashi da makami da barayin shanu saboda kusancinmu da jihohin Katsina da Zamfara.” Inji Dr.Mani Tsoho.

Cushe: Hatsaniya ta kaure a Majalisar Dattawan Nigeria

A Cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na shiyyar Gwarzo Rabi’u Khalil ya aikowa kadaura24, yace kantoman ya yi alkawarin bayar da cikakken goyon baya ga dukkan jami’an tsaro da ke aiki a yankin domin gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

A nasa bangaren daraktan kula da ma’aikata na karamar hukumar Ubale Magaji ya taya kwamitin riko a karkashin jagorancin Dr.Mani Tsoho Gwarzo murna tare da godewa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa zabar yan kwamitin.

Yadda Mace ta Farko da Gwamnan Kano Ya Baiwa Kantoma Ta Sha Alwashi

A nasa jawabin Hakimin Gwarzo Barde Kerarriya Alh. Kabiru Bayero ya yi kira ga mukaddashin shugaban kwamitin rikon da ya kara kaimi kan nasarorin da gwamnatin da ta shude ta samu kan harkokin tsaro.

Alh.Kabiru Bayero yayin da yake taya su murna ya kuma yi alkawarin tallafa wa dukkanin masu rike da sarautun gargajiya da na addini.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu:yanzu: Gwamnan kano ya yi sabbin nade-naden mukamai

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Gwamann jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Daga Fatima Mahmoud Diso   Shugabanni da jagororin jam'iyyar APC na...