Ramadan: Ku yiwa Nigeria addu’o’i don ta fita daga mawuyacin halin da take ciki – Minista ATM Gwarzo

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Karamin ministan gidaje da raya birane na Nigeria Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo ya yi kira ga al’ummar Musulmin Nigeria da su dage da rokon Allah ya magance matsalolin da suka dabaibaye Kasar .

Ministan ya yi wannan kiran ne a cikin sakonsa na taya Musulmi Murnar zagayowar azumin watan Ramadan, wadda mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai Adamu Abdullahi ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.

Cushe: Hatsaniya ta kaure a Majalisar Dattawan Nigeria

A cewarsa, “watan Ramadan daya ne daga cikin lokuta masu alfarma a Musulunci inda al’ummar Musulmi a fadin duniya suke gudanar da ibadu domin neman yardar Allah Subhanahu wata’ala, don ya ce yiwa Nigeria addu’a a wannan lokaci yana da matukar muhimmaci.

Zamu fi Baiwa Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Al’ummar Gwarzo Fifiko – Kantoman Gwarzo

Ya kuma yi kira ga daukacin musulman Nijeriya da su yi amfani da wannan damar wajen gudanar da addu’o’in samun zaman lafiya, ingantuwar tattalin arziki da kuma ci gaban kasa.

Minista Gwarzo ya kuma yi kira ga Limamai da Malamai da su yi amfani da wuraren wa’azi da tafsirinsu don sanar da al’umma muhimmancin zaman lafiya da hadin kai a tsakanin ‘yan Nijeriya.

Ramadan: Dan Majalisar Bichi ya kaddamar da rabon Abinchin da ba’a taba yin irinsa ba a Kano

Ministan, yayin da yake bayyana damuwarsa kan halin tsaro da tabarbarewar tattalin arzikin da ake fama da shi a kasar, ya bukaci ‘yan Najeriya da su hada kai da gwamnatin tarayya karkashin jagorancin shugaba Bola Ahmad Tinubu wajen marawa manufofin gwamnatin bayan don warware matsalolin da Kasar take ciki.

Minista Gwarzo, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmi da su yi amfani da lokacin Azumin watan Ramadan domin neman taimakon Allah a kan kalubalen da kasar ke fuskanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...