Ramadan: Dan Majalisar Bichi ya kaddamar da rabon Abinchin da ba’a taba yin irinsa ba a Kano

Date:

Daga Nafisa Abdullahi Bichi

 

Dan Majalissar tarayya mai wakiltar Bichi kuma Shugaban Kwamitin kasafi na Majalissar tarayya, Hon. Abubakar Kabir Abubakar ya kaddamar da rabon kayan kayan abinchi don tallafawa al’ummarsa sakamakon shigowar azumin watan Ramadan.

An dai fara raba kayan abinchi ne a ranar Lahadin data gabata,inda aka fara da Mazabun Yallami da Kwamarawa duk a Karamar hukumar ta Bichi.

A Cikin wata sanarwa da mai taimakawa dan majalisar kan harkokin yada labarai Jamilu Halliru Master ya fitar, yace Alhaji Kabir Abubakar Kabir dama ya saba raba irin waɗannan kayan abinchi a duk lokaci irin wannan na azumi.

Yadda za ku kula da kanku a lokacin azumin Ramadan

Sanarwar tace ana a bana za’a baiwa magidanta babban buhun shinkafa mai nauyin 50kg, saboda saukakawa al’umma sakamakon halin matsin tattalin arzikin kasa ake fuskanta a bana.

A jawabinsa, shugaban ma’aikatan Ofishin Dan Majalissar Hon. Sabo Iliyasu Saye wanda shi ne ya wakilci dan majalissar yayi kira ga al’ummar da suka rabuta da wannan abinci da suyi amfani da shi yadda ya dace, domin samun nasarar da ta aka raba abinchin.

Yadda Gobara ta tashi a tashar wutar lantarki ta Dan agundi dake Kano

“Dan majalissar tarayyar mu Hon. Abba Bichi a shirye yake ya cigaba da taimakawa al’ummar Karamar Hukumar Bichi yadda ya kamata kamar yadda ya saba”.

” Saboda yanayin da ake ciki Hon. Abba Bichi ya ce a bana kowacce Akwatu da muke da ita a karamar hukumar Bichi za’a baiwa magidanta 100 buhun shinkafa don tallafa musu, a wannan wata mai albarka”.

Taron ya samu halartar daukacin Ma’aikatan Dan Majalissar Tarayya, shugabannin Jam’iyyar APC na Karamar Hukumar Bichi da sauran Al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Daga Fatima Mahmoud Diso   Shugabanni da jagororin jam'iyyar APC na...

Kotu ta ɗaure wani ɗan Tiktok mai wanka a tsakiyar titunan Kano

    Wata kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya...

Damuna: Mun shirya inganta wuraren tsayarwar motocinmu – Kungiyoyin Direbobin na Kano

Kungiyar matuka motocin kurkura ta jihar Kano da Kungiyar...