Kwankwaso Zai Bude Asibitin Kangararru a Kano

Date:

Daga Usman Hamza

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Engr. Rabiu Kwankwaso zai kaddamar da asibitin kangararru mai zaman kansa, da kuma kula da Masu lalurar damuwa a jihar Kano.

Cibiyar Mai Suna Amana Sanatorium a rikunin Gidaje na jido dake Kano, za a kaddamar da ita a ranar 21 ga Oktoba, 2021, a wani bangare na bikin cika Sanata Rabiu Musa Kwankwaso Shekaru 65 a Duniya.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai taimaka wa kwankwasiyya Kan harkokin kafafen yada labarai Ibrahim Adam ya fitar a ranar Asabar din nan.

Sanarwar ta bayyana cewa Idan za’a iya tunawa a shekarar 2011 lokacin da Sanata Rabiu Kwankwaso ya dawo wa’adi na biyu na Gwamnan Kano, ya gano an Sami l karuwar masu shan miyagun kwayoyi, ‘yan daba da marasa aikin yi.

” Matasa da yawa ‘yan siyasa na amfani da su a matsayin yan barandan siyasa, kuma basu da aikin yi sai jagaliya a ofisoshi gwamnati don neman tsira da rayuwarsu, ” in ji sanarwar.

A cewar sanarwar, wannan ya sa tsohon Sanatan Kano ta tsakiya, Rabiu Kwankwaso, ya kafa kwamitin da zai yi yaki da haramtattun dillalan miyagun kwayoyi da masu shan muggan kwayoyi a jihar Kano a wancan Lokacin.

” Ya kafa cibiyar koyar da harkokin tsaro, duk don rage shan miyagun ƙwayoyi, sece-sace da rashin aikin yi ga matasa marasa ilimi a Kano. ”

” An kafa cibiyar gyara ne don ceto Matasan da suke Shan muggan Kwayoyi domin su zamo Masu amfanar kansu da Kuma al’umma, Sannan Kuma a rage yawan laifuffuka a Kano.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...