Daga Abubakar Lawan Bichi
Kungiyar jama’atu Nasril Islam reshe Karamar hukumar Bagwai ta shirya taro masu ruwa da tsaki domin kawo masalaha yayi gudanar aure a dukkan fadi Karamar hukumar ta Bagwai.
Madawakin Bichi hakimin na Karamar hukumar ta Bagwai Alh Nura Shehu Ahmad ne ya jagoranci taron .
Masu ruwa da tsaki sun hada da dagatai, masu Unguwani da Limamai manyan mallamai addinin Musulunci dake fadin ta Karamar hukumar ta Bagwai.
Hukumar Gidan Gyaran Hali ta Kano ta Magantu Kan Bacewar Murjar Kunya a Gidan Yari
A wata makalar daya gabatar akan Mahimmanci Aure tsakani Mijin da Mata a Shari’ar musulunci da Kuma waya kamata ya Samar da kayan daki a Sharia musulunci yayi gudanar da aure Gabatar Babban Limamin garin Kiyawa dake Karamar hukumar ta Bagwai Mallam BILYAMINU Abubakar yace ayyoyin Qur’an da hadisan manzo Allah (s a w) nauyi da Sharia musulunci ta daurawa Ma’aurata.
Kano: NAFDAC da Gargaɗi Kamfanoni Game da Yan Kasuwar Magani na Sabon Gari
Dan Majalisar Koli na Kwamiti Jama’atu Nasril Islam na Karamar hukumar ta Bagwai Wanda Kuma shi ne Na’ibi Limamin Juma’a na Karamar hukumar Bagwai Mallam Sani Musa Bagwai ya bayyana cewa an shirya taron ne domin tattauna hanyoyi Samar da masalaha tsakani bangarorin masu masu aure a fadi Karamar hukumar ta Bagwai.
Mallam Aminu Yusuf Bagwai shi ne wakilin Kungiyar Kadiriya a Kwamiti ya bayan Mahimmanci bin tsarin addini musulunci yayi gudanar da aure, Inda yace matukar akabi tsari da Musulunci ya zo da shi wajen aure za’a sami saukin wahalhalun da aka fuskanta.
Yace Kwamiti na Jama’atu nasril Islam zai kawo dedeto a dukkan sukar aure a fadi Karamar hukumar ta Bagwai.
Taro ya Sami halartar dukkan dagatai masu Unguwani da Limamai dake Karamar hukumar ta Bagwai.