Gwamnatin Kano Ta Ayyana Ranar Hutun Mauludi

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana gobe Juma’a, 12 ga Satumba, 2025, wanda ya yi daidai da 19 ga Rabi’ul Awwal 1447 bayan hijira, a matsayin ranar hutu domin bikin Mauludin haihuwar Annabi Muhammad (SAW).

A cikin sanarwar da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya ya sanya wa hannu a ranar Alhamis, gwamnati ta bukaci ma’aikata, ‘yan kasuwa da kuma al’ummar jihar su gudanar da hutun cikin lumana tare da bin koyarwar Annabi Muhammad (SAW).

Sanarwar ta kuma yi kira ga jama’a da su yi amfani da wannan damar wajen tunawa da darussa na haɗin kai, juriya da biyayya da kuma koyi da halayen Annabi Sallallahu alaihi wasallam.

Hasashe 6 da Musa Iliyasu Kwankwaso ya yi kuma suka tabbata a siyasar Kano

Haka zalika, gwamnatin ta shawarci al’ummar jihar da su yi addu’o’i na musamman domin Allah ya baiwa jihar Kano da Nigeria baki daya zaman lafiya da karuwar tattalin arziki.

FB IMG 1753738820016
Talla

Gwamnatin jihar ta kuma taya al’ummar Kano murnar bikin Mauludi tare da fatan za a gudanar da shi cikin kwanciyar hankali da lumana .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...