Yadda Masu Ababen Hawa a Kano Ke Zargin Jami’an KAROTA da Rokon su Kuɗi

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Masu ababen hawa da ke bin manyan tituna a jihar Kano sun nuna damuwarsu kan yadda jami’an hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Kano, KAROTA ke yawan rokon su kuɗi .

Jami’an KAROTA na yin shingaye a kan tituna a jihar yayin da wasu kuma suke tsayawa a hanyoyin gwamnatin tarayya da suka hada Kano da sauran jihohin.

Jami’an KAROTA yawanci suna tare hanya da tsofaffin tayoyi tare da jami’ansu wajen cin zarafi da karbar Kudade a wajen masu motoci.

Bayan Zanga-Zangar Lumana, Masu Sana’ar Gurasa a Kano Sun Bayyana Dalilan su na Tafiya Yajin Aiki

Hanyoyin da suka yi kaurin suna wajen ganin ayyukan KARATO sun hada da Maiduguri, Hadejia, Gwarzo, Zaria da Katsina Road, wadanda suka hada Kano da sauran jihohin da ke makwabtaka da su.

Wasu daga cikin masu ababen hawa da suka zanta da manema labarai bisa sharadin sakaye sunansu, sun ce a kullum sai sun tanadi kudin da zasu baiwa yan KAROTA domin gujewa cin zarafi daga gare su.

“Muna bayar da makudan kudade ga jami’an KAROTA wadanda suke tare manyan shingaye kan manyan tituna suna karbar kudi daga wajenmu ba tare da sanin wasu dalilai ba.

Jaruma Amal Umar ta Bayyana Alakarta Da Mawaki Umar M Shariff

A lokacin da tawagar ‘yan jarida ta ziyarci ofishin Manajan Daraktan KAROTA Faisal Muhmud domin tabbatar da zargin da ake yi musu, ya ki ya gana da yan jaridun, amma wani ma’aikacin ofishin da ya so a sakaya sunansa ya ce MD ba ya jin dadin yan jaridu suke zuwa Ofishin nasa domin tattaunawa da shi.

 

Daily Post 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...