Da dumi-dumi : Kotu Ta Bayyana Dalilin Mayar da Danbilki Kwamanda Gidan Yari

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

An koma da Danbalki kwamanda Zuwa gidan Kurkuku Sakamakon Alƙalin da ke shari’ar bashi da lafiya saboda haka ba zai iya sauraren karar ba a yau, Don haka an ɗage shari’ar har zuwa ranar Alhamis mai zuwa.

Gwamnatin kano ce ta gurfanar da Kwamanda a gaban Kotun Sakamakon Zargin kalaman tunzura jama’a domin yin tawaye ga gwamnatin jihar Kano akan lamarin da ya shafi Masarautun jihar kano.

Dalilan da Suka sa Likitoci Suka Dakatar da Aiki a Asibitin Murtala na Kano

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa a makon da ya gabata aka gurfanar da Danbilki Kwamanda a gabon kotun majistiri dake Noma’s Land, inda bayan sauraron karar kotun ta aike da shi gidan yari har zuwa wannan rana domin cigaba da sauraron karar.

Danbilki Kwamanda dai yayi kaurin suna wajen kalubalantar manufofin gwamnatin jihar Kano da kuma jagoran darikar Kwankwasiyya Engr. Rabiu Musa Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...