Da dumi-dumi : Kotu Ta Bayyana Dalilin Mayar da Danbilki Kwamanda Gidan Yari

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

An koma da Danbalki kwamanda Zuwa gidan Kurkuku Sakamakon Alƙalin da ke shari’ar bashi da lafiya saboda haka ba zai iya sauraren karar ba a yau, Don haka an ɗage shari’ar har zuwa ranar Alhamis mai zuwa.

Gwamnatin kano ce ta gurfanar da Kwamanda a gaban Kotun Sakamakon Zargin kalaman tunzura jama’a domin yin tawaye ga gwamnatin jihar Kano akan lamarin da ya shafi Masarautun jihar kano.

Dalilan da Suka sa Likitoci Suka Dakatar da Aiki a Asibitin Murtala na Kano

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa a makon da ya gabata aka gurfanar da Danbilki Kwamanda a gabon kotun majistiri dake Noma’s Land, inda bayan sauraron karar kotun ta aike da shi gidan yari har zuwa wannan rana domin cigaba da sauraron karar.

Danbilki Kwamanda dai yayi kaurin suna wajen kalubalantar manufofin gwamnatin jihar Kano da kuma jagoran darikar Kwankwasiyya Engr. Rabiu Musa Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta nemi majalisar dokokin jihar ta haramta auren jinsi

Gwamnatin jihar Kano ta buƙaci majalisar dokokin jihar ta...

Yan sanda a Kano sun lashi takobin samar da ingantaccen tsaro a ranar Takutaha

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori,...

Gwamnatin Kano Ta Ayyana Ranar Hutun Mauludi

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana gobe Juma’a, 12 ga...

INEC ta yi Allah-wadai da masu yakin neman zabe tun kafin lokaci ya yi

Hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC) ta yi Allah wadai...