Da dumi-dumi : Kotu Ta Bayyana Dalilin Mayar da Danbilki Kwamanda Gidan Yari

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

An koma da Danbalki kwamanda Zuwa gidan Kurkuku Sakamakon Alƙalin da ke shari’ar bashi da lafiya saboda haka ba zai iya sauraren karar ba a yau, Don haka an ɗage shari’ar har zuwa ranar Alhamis mai zuwa.

Gwamnatin kano ce ta gurfanar da Kwamanda a gaban Kotun Sakamakon Zargin kalaman tunzura jama’a domin yin tawaye ga gwamnatin jihar Kano akan lamarin da ya shafi Masarautun jihar kano.

Dalilan da Suka sa Likitoci Suka Dakatar da Aiki a Asibitin Murtala na Kano

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa a makon da ya gabata aka gurfanar da Danbilki Kwamanda a gabon kotun majistiri dake Noma’s Land, inda bayan sauraron karar kotun ta aike da shi gidan yari har zuwa wannan rana domin cigaba da sauraron karar.

Danbilki Kwamanda dai yayi kaurin suna wajen kalubalantar manufofin gwamnatin jihar Kano da kuma jagoran darikar Kwankwasiyya Engr. Rabiu Musa Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...