Ba zamu lamunci yadda ake yada dokokin karya na Hukumar mu ba – KAROTA

Date:

 

 

Hukumar Kula da Zirga zirgar Ababen Hawa ta jiha KAROTA ta karyata wani rubutu da ta gani yana yawo da sunan Hukumar.

Shugaban Hukumar KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ne ya karyata hakan, bayan da aka kula da rubutun yana yawo a Soshiyar Midiya wanda aka yi masa suna da “SABABBIN DOKOKIN HUKUMAR KAROTA”.

Jarumar Hadiza Gabon Ta Yi Martani ga Masu Magana Kan Ramarta

Hukumar ta ce wannan rubutu da ke kunshe a cikin Soshiyar Midiya baya cikin Sabbin Dokokin da aka sabunta a shekara ta 2022 na kundin dokar da ta kafa KAROTA a shekara ta 2012.

An rantsar da Ododo a matsayin sabon gwamnan Kogi

Hukumar ta ce za ta ci gaba da kama tare da gurfanar da wadanda suke yada rubuce-rubucen karya da sunan Hukumar wajen jami’an Yan sanda.

Tuni Hukumar tare da jami’an tsaro suka dukufa wajen nemo waðanda suke yada jita-jitar tare da gurfanar da su a gaban Shari’a.

A karshe Hukumar ta ce ta kusa kammala shirinta na fassara sabuwar Dokar Hukumar da aka sabunta a shekara ta 2022 wadda za a fassarata zuwa harshen Hausa domin saukakawa jama’a fahimtar abinda ke kunshe a cikin sabuwar dokar

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...