Tinubu Ya Magantu Kan Batun Dauke Fadar Shugaban Kasa Daga Abuja

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Mai bai wa shugaban Najeriya Bola Tinubu shawara kan yada labarai, Bayo Onanuga ya ce shugaban kasar ba shi da aniyar ɗauke babban birnin tarayyar ƙasar daga Abuja zuwa Legas.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, ranar Laraba, Onanuga ya ce masu yada jita-jita ne ke yaɗa maganar domin jan hankalin al’umma gare su.

Hukumar Hisbah Tana Neman Wasu Taurarin TikTok Guda 6 Ruwa a Jallo

Wannan na zuwa ne bayan matakin da gwamnatin tarayyar ƙasar ta ɗauka na mayar da wasu ɓangarori na Babban bankin Najeriya da kuma Hukumar kula da filayen jiragen sama na ƙasar zuwa Legas, daga Abuja.

Lamarin da ya janyo ƙorafi da kiraye-kiraye daga wasu ƙungiyoyi na wasu ɓangarorin ƙasar, inda suka yi zargin cewa tamkar wani mataki ne aiwatar da wata ‘manufa ta daban.’

Hadewar NNPP Kwankwasiyya da APC a Kano Sabuwar Dambarwar Siyasa ta Kunna Kai

Onanuga ya ce matakin mayar da wani sashi na ma’aikatar FAAN bai kamata ya ja hankalin mutane da yawa ba saboda jihar Legas ita ce cibiyar kasuwanci kuma cibiyar sufurin jiragen sama a Najeriya saboda haka ya ce har yanzu FAAN za ta ci gaba da kasancewa a Abuja.

“Akwai ma’aikatu da yawa da ba a Abuja suke ba dangane da aikinsu kamar NIMASA da take Legas. Haka kuma NPA da kuma hukumar kula da sufurin ruwa (NIWA) da ke Lokoja.’

Sanarwar dai ta ƙara da cewa bai kamata a siyasantar da lamurran gwamnati ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...

Bayan Amincewar Kasar Saudia , an Sanya Ranar Binne Aminu Dantata a Madina

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid...

Rashin Alhaji Aminu Dantata Babban Rashi ne ga harkokin kasuwanci a Duniya – Salbas

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Babban kamfani a masana'antar mai a...

NNPPn Kano ta bayyana matsayar Kwankwaso kan batun yi wa Tinubu mataimaki a 2027

Shugabanin bangarori biyu na jam’iyyar NNPP a jihar Kano,...