Abba Gida-gida ya Fadi Rawar da Kwankwaso ya Taka a Shari’ar Zaɓen Gwamnan Kano

Date:

 

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya tabbatar da cewa ba zai taba cin amanar mai gidansa, tsohon gwamnan jihar, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ba.

Da ya ke jawabi ga magoya baya a Abuja, jim kaɗan bayan yanke hukuncin Kotun Ƙoli da ta tabbatar masa da zaɓen sa, Gwamna Yusuf ya nuna godiya ga Kwankwaso bisa kwazonsa na ganin cewa ba a zalunci al’ummar Kano ba.

A cewar Gwamna Yusuf; ” mu na godiya ga Allah da wannan gagarumar nasara da ya bamu. Mu na kuma godiya ga jagoran mu, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso bisa kwazonsa na ganin cewa ƙuri’un da aka awa su ka kada ba a kwace musu ba.

Kyautar Motar da aka Baiwa Jarumar Labarina Yasa Marubutan Kannywood Kokawa

“Hakika Kwankwaso jagora ne kuma mu na alfahari da shi. Za mu ci gaba da yin biyayya kuma ba za mu taɓa cin amanar sa ba,” in ji Gwamnan.

Jirgi ya yi saukar gaggawa bayan fasinja ya gartsa wa ma’aikaciya cizo

Ya kuma godewa shugaban ƙasa Bila Tinubu da mataimakin sa, Kashim Shettima bisa nuna dattaku na kin saka baki a shari’ar, inda ya ce hakan ya kara wa kasar da kuma dimokuraɗiyya kima a idon duniya.

Gwamnan ya kuma godewa alkalan Kotun Ƙoli bisa abinda ya kira da “adalci wajen ganin sun baiwa mai gaskiya gaskiyar sa. Hakan zai kara gyara harkar zabe da dimokuraɗiyya a kasar,”

“Mu na matukar godiya ga al’ummar Kano bisa wannan soyayya da ake nuna mana. In sha Allah za mu bijiro da aiyukan alheri da za su kara habbakar arziki da ci gaba a jihar mu. Mun gode muku sosai,” in ji Gwamnan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...