Zargin Bata Suna: An Gurfanar da Mai Magana da Yawun AA Zaura a Gaban Wata Kotu a Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

An gurfanar da Ahmad Dahiru Maiwuddadu, wanda ya rike mukamin kakakin Abdussalam Abdulkarim A.A Zaura, dan takarar kujerar Sanatan Kano ta tsakiya a zaben da ya gabata, a gaban babbar kotun majistare ta jihar Kano mai lamba 19.

Ana zarginsa da bata sunan Sanata Rufa’i Hanga mai wakiltar Kano ta tsakiya a Majalisar Dattawa ta kasa da kuma tada hankalin jama’a.

Justice watch ta rawaito ana zargin Maiwuddadu da bata sunan Sanata Hanga a wani shiri na gidan rediyo mai taken ‘Tauraron A.A Zaura’ wanda A.A Zaura ya dauki nauyi.

Kyautar Motar da aka Baiwa Jarumar “Labarina” Yasa Marubutan Kannywood Kokawa

Mai gabatar da kara, Barista Fatima Adamu Ahmad, ta yi zargin cewa wanda ake karar ya kira Sanata Hanga a matsayin mashayin giya wanda ya wawure kudin mazabar karamar hukumar birni tare da kashe su a gidajen giya.

Mai gabatar da kara ta bayyana cewa wadannan laifukan da ake zargin maiwuddadu sun sabawa sashe na 393 da 144 na dokar manyan laifuka.

Sai dai Maiwuddadu ya musanta aikata laifukan.

A zaman kotun, lauyan da ke kare Wanda ake tuhuma Anthony Agugu ya bukaci kotun da ta bayar da belin Maiwuddadu, bisa la’akari da wasu sassan na kundin tsarin mulkin Najeriya da ya ambato da kuma dokar shari’a ta jihar Kano, 2019.

Jirgi ya yi saukar gaggawa bayan fasinja ya gartsa wa ma’aikaciya cizo

Lauyan mai gabatar da kara bai soki bukatar belin ba, inda yace bayar da belin ikon kotun ne kadai.

Alkalin kotun, Binta Galadanchi, ta bayar da belin wanda ake kara a kan kudi naira dubu dari biyu, tare da wasu amintattun mutane biyu wadanda za su kasance ma’aikatan gwamnati masu Matakin albashi na 12 da kuma hakimin ko Unguwa.

Daga nan mai Shari’a Binta Galadanci ta dage sauraren karar har zuwa ranar 29 ga Fabrairu, 2024, don ci gaba da Shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...