Sarkin Kano Ya Magantu Kan Nasarar Gwamna Abba Kabir a Kotun Ƙoli

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya taya gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf murnar nasarar da ya samu a kotun koli.

Sarki Alhaji Aminu Ado Bayero ya ce hukuncin kotun koli nuni ne na zabin mutane da kuma dimokuradiyya da kuma shugabanni na kwarai da masu biyayya ga abin da masu zabe za su yi.

Wani Mawaki a Kano ya Maka BBC Hausa a Kotu

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran masarautar kano, Abubakar Balarabe kofar Na’isa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.

Yanzu-yanzu: Barawon da ya kwaci waya Mota ta buge shi a Kano ya mutu – Yan sanda

A cewar sanarwar dake kunshe ta taya murna, Sarkin ya yabawa al’ummar jihar Kano bisa zabin da ya dace wanda zai tabbatar da ci gaba da tsare-tsare na cigaban jihar.

Daga karshe ya yi addu’ar Ubangiji Allah ya kare shi daga makiya na zahiri da badini, ya kuma ba shi kwarin guiwar cika alkawura da kuma gudanar da ayyukansa cikin himma da nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...